Mace ko Namiji wadanda basu samu haihuwa ba, ga wata Fa’ida nan mai girma daga SIRRIN MA’AURATA, don haka saiku jarraba za’a samu dacewa insha Allahu.

1. Garin Habbatus Sauda cokali 5.
2. Garin ‘ya’yan Fijil Cokali 5.
3. Garin ‘Ya’yan Hulba cokali 5.

Ahadasu gaba daya a gauraya sannan a zuba cikin Zuma kofi daya. Sai a rika shan cokali guda daya, safe da yamma.

Sannan abi bayansa da kofi guda na Nonon rakumi.

Insha Allahu za’a samu haihuwa.

Idan Namiji ne, koda ‘Ya’yan maniyyinsa ne suka mutu, to insha Allahu, Allah zai raya su.

Idan kuma Mace ce, koda tana da wasu cututtuka a cikin mahaifarta, to insha Allahu zata samu waraka, kuma zata haihu.

Idan an gwada kuma an dace, tukwicin shine AYI GODIYA GA ALLAH.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *