A mafi yawancin lokuta ana samun daukewar ni’ima bayan mace ta haihu, wanda hakan yana jawo kyamata ko kuma nuna rashin halin ko’in kula a gareta daga mijin ta. Wannan tana faruwa ne a lokacin da maigida ya kwanta dake, inda ba zaiji wani dandano daga gareki ba.

Wannan yanayi ba karamin jefa mace halin damuwa yake ba, musamman idan taga yadda mijin ta yake nuna mata wani hali na daban, domin ba kowanne maigida bane zai fada miki abinda yake ji a lokacin da kuke raya sunnah.

To a duk lokacin da irin haka ta faru, sai ki nemi wadannan abubuwan da zan lissafo domin samarwa kanki lafiya.

Abubuwan da zaki nema sune kamar haka :

– Sassaken kankana
– Sassaken baure
– Ya’yan zogale
– Idon zakara
– Asuwakin mata
– Ganyen kafi suga

Yadda za’a hada :

Ki hada ki dake ki tankade yayi laushi sossai ki dinga zuba cikin cokali abinci daya cikin madara shanu kofi daya ko cikin madarar ruwa gwangwani daya kina sha safe da yamma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *